*Fita Na hudu. GHADEER KUM: WAYE SHUGABAN MUSULMI BAYAN WAFATIN MANZON ALLAH??*
_Daga: Muh'd Jawad Assaminaky_ Tabbas Manzon Allah Bai Bar Duniya ba Sai daya Nuna Mana Magaji a Bayansa! Saboda an dora masa wani takhlifi, sai ya je wani wuri wanda idan wata masifa za ta sami mutanen Makka, misali ko yaki ko wani bala'i, in ka je ka yi kururuwa ko ka daga sauti ka yi kira, to an san akwai wata magana, watakila an kawo yaki ko wani abu. Da isarsa sai ya hau, yana hawa sai ya ce "ya bani Hashim! Ya bani Abdulmutallib! Ya bani Tim! Ya banu.."/Nan da nan jama'a suka cika wurin makil ya ce musu:"Idan na ba ku labari za ku gaskata? Suka ce haba ya Muhammad! Ya za a ce ba za mu gaskata ka ba! Bayan ba mu taba samun ka da karya ba." Sai ya ce, "in na ce muku yanzu akwai a bayanBgarin nan mayaka sun taru za su yake ku duk da ba ku gani ba za ku yarda? Suka ce, "za mu yarda, me zai hana? Sai yake cewa, "to ni din nan Manzon Allah ne (S). Daga nan fa sai suka ce "assha! Tir! Don haka ne ma ka tara mu? Sai ya ci gaba da ce...