SHAFI (1) ABUBUWAN DA ZA MU KOYA DAGA RAYUWAR SAYYADA ZAHRA (AS)
Da sunan Allah mai rahama mai jinkai. Tsira da aminci su kara tabbata ga Manzon rahama Muhammad dan Abdullahi da Iyalan gidansa tsarkaka, taurarin duniya da lahira da Sahabbansa managarta. Nazari da bincike a kan rayuwar Sayyadah Zahra abu ne faffada ainun, wanda za mu iya misalta shi da iyo a teku. Amma za mu yi ne da nufin bijiro da yadda rayuwarta ta kasance don daukar darussan da ke cikinta, haka kuma don mu sanya ta a matsayin samfuri ga rayuwar Musulmi baki daya. Ta yadda za mu fahimci manufar rayuwarmu wadda domin ta ne Allah ya halicci dan Adam. An haifi Fatimatuz Zahra ne ranar Juma’a 20 ga watan Jimada Thani a shekara ta biyar bayan wahayi. Mahaifinta shi ne Manzon Allah Muhammad dan Abdullahi, cikamakon Annabawa da Manzanni, rahama ga talikai. Mahaifiyarta kuwa ita ce; Nana Khadijatul Kubra (AS) matar Manzo (S) ta farko, wacce ta fara amsa kiran Manzo. Sannan kuma ta bai wa wannan addini muhimmiyar gudummawar da ba za a taba mantawa da ita ba har abada. Manzo (S) ya ce...