Posts

KISA BA'A BISA KA'IDABA

Image
  Sojojin Mamayan Haramtaciyar kasar Isra'ila sun kashe matashin yaro Bafalasdine Dergham Al-Akhras Mai Shekaru 19 a samamen da suka Kai da Safiyar Yau Laraba a Sansanin'yan gudun Hijira na Aqabat Jabr a ga6ar Yammacin kogin Jordan. #Islamicnewupdate #PalestineAyau

WAFATIN UMMUL BANIN MAHAIFIYAR ABUL FADLIL ABBAS!

Image
  Bismillahirrahmanirrahim 13 ga Watan Jumadat-Thaniyah. A irin wannan rana ce a Shekara ta 65 bayan hijirah, a ranar Juma'a, Allah ya karbi ran Ummul Banin (S.A), Mata a wajen Imamu Ali alaihissalam kuma Mahaifiyar Abul Fadlil Abbas Jarumin Karbala!. Tsarkakken Makwancinta yana nan a ciki Makabartar Baqi'a, a kusurwar bangaren hagu kusa da Makwancin Sayyid Ibrahim Dan Ma'aiki (Saww), da Zainab da Ummul Kulthum da Abdullahi da Kasim, amincin Allah ya kara tabbata a gare Su. WACE CE UMMUL BANIN (S.A)?   Zanannen Sunanta Shi ne Fadimatu 'Yar Hizam. Mahaifiyarta kuwa ita ce: Thumamah bnt Sahal bn Amir bn Malik bn Ja'afar bn Kilab.  Ta kuma Shahara da Lakabin Ummul Banin, kuma an ce Imamu Ali (as) ne da kansa ya kira ta da laqabin na Ummul banin. AURENTA DA IMAMU ALI (AS). Malaman Tarikhi sun ruwaito cewa Imamu Ali (as) ya sanya Dan uwansa Aqil ne da ya nemo masa wata Mace Jaruma daga Gidan Jarumawan Kabilun Larabawa domin ta haifa masa Jarumin da zai agaza wa Dansa Hus...

SYED MOJTABA HUSSAIN ALI KHAMNAE (DZ).

Image
  Ɗa ne ga Syed Ali Khamanei, Mahafiyarsa kuma Mansoureh Khojaste Bagherzadeh, an haife shi ranar 8 ga watan Satumba, 1969, yana da Shekaru 54 yanzu a duniya.  Ya Halarci yaƙin Iran da Iraq, wadda Saddam ya sabbaba shi a Shekarar 1987-1988, yanzu haka shi Kwamanda ne a wani sashen rundunar mayakan sa-kai na Iran wato Basij. Malumansa sune... Syed Ali Khamenei (DZ) Syed Mahmoud Hashemi Shahroudi Sheikh Mohammad-Taqi Mesbah-Yazdi Sheikh Lotfollah Safi Golpaygani Syed Mohammad Bagher Kharazi. Yana da yara 3, a matakin karatunsa na Hauza Ayatullahi ne. Allah ya ƙarawa Maraji'anmu da Iyalan su damu kammu Almajiransu Albarka. Bada bayani daga  Muhd Bala Afuwa

دعاء المشلول‌

 د عاء المشلول‌ اللّهُمَّ إِنِّي‌ أَسْئَلُكَ بِاسْمِكَ بِسْمِ اللهِ الرَّحْمنِ الرَّحِيمِ يا ذَا الجَلالِ وَالإِكْرامِ يا حَي‌ُّ يا قَيّومُ لا إِلهَ إِلاّ أَنْتَ يا هُوَ يا مَنْ لا يَعْلَمُ ما هُوَ وَلا كَيْفَ هُوَ وَلا أَيْنَ هُوَ وَلا حَيْثُ هُوَ إِلاّ هُوَ يا ذَا المُلْكَ وَالمَلَكُوتِ يا ذا العِزَّةِ وَالجَبَرُوتِ يا مَلِكَ يا قُدُّوسُ يا سَلامُ يا مُؤْمِنُ يا مُهَيْمِنُ يا عَزِيزُ يا جَبارُ يا مُتَكَبِّرُ يا خالِقُ يا بارِئُ يا مُصَوِّرُ يا مُقَدِّرُ يا مُفِيدُ يا مُدَبّرُ يا شَدِيدُ يا مُبْدِئُ يا مُعِيدُ يا مُبِيدُ يا وَدُودُ يا مَحْمُودُ يا مَعْبودُ يا بعِيدُ يا قَرِيبُ يا مُجِيبُ يا رَقِيبُ يا حَسِيبُ يا بدِيعُ يا رَفِيعُ يا مَنِيعُ يا سَمِيعُ يا عَلِيمُ يا حَكِيمُ يا حَلِيمُ يا كَرِيمُ يا قَدِيمُ يا عَلِي‌ُّ يا عَظِيمُ يا حَنّانُ يا مَنّانُ يا دَيانُ يا مُسْتَعانُ يا جَلِيلُ يا جَمِيلُ يا وَكِيلُ يا كَفِيلُ يا مُقِيلُ يا مُنِيلُ يا نَبِيلُ يا دَلِيلُ يا هادِي‌ُ يا بادِي‌ يا أَوَّلُ يا آخِرُ يا ظاهِرُ يا باطِنُ يا قَائِمُ يا دآئِمُ يا عالِمُ يا حاكِمُ يا قاضِي‌ يا عادِلُ ي...

Hadith Aqa'ed

 Aqaed (Qayamat [Alqiyamah])  Imam Sadik (as) ya ce  A ranar kiyama za a gurfanar da mutane  kamar haka.  Wanda yayi namaz a rayuwarsa.  Da a ce masa ka yi addu'a, amma nufinka ya kasance don nuna bayyani ne, domin mutane su yaba ibadarka.  Za a jefa wannan mutum cikin wuta.  Sai a kawo mai karatun Alqur'ani.  Za a ce masa, 'a lokacin da kake karatun Alqur'ani, nufinka shi ne ka baje kolin sautinka mai dadi domin mutane su yaba sautin ka.  Wannan kuma za a jefa shi cikin wuta.  Mutum na uku da za a gabatar shi ne wanda ya yi shahada a jihadi.  Sai a ce masa: “Niyyarka a lokacin da kake yaqi ita ce ka nuna qarfinka da bajinta.” Kuma a kai shi zuwa ga wuta.  a cikin yin sadaka, domin mutane su ce ka mai karimci ne.  Sa'an nan kuma a kai shi zuwa Jahannama.  Manyan Zunubai Vol 1, Sashe na 3, shafi na 76;  Layali Akhbaar

SHAFI (1) ABUBUWAN DA ZA MU KOYA DAGA RAYUWAR SAYYADA ZAHRA (AS)

Image
  Da sunan Allah mai rahama mai jinkai. Tsira da aminci su kara tabbata ga Manzon rahama Muhammad dan Abdullahi da Iyalan gidansa tsarkaka, taurarin duniya da lahira da Sahabbansa managarta. Nazari da bincike a kan rayuwar Sayyadah Zahra abu ne faffada ainun, wanda za mu iya misalta shi da iyo a teku. Amma za mu yi ne da nufin bijiro da yadda rayuwarta ta kasance don daukar darussan da ke cikinta, haka kuma don mu sanya ta a matsayin samfuri ga rayuwar Musulmi baki daya. Ta yadda za mu fahimci manufar rayuwarmu wadda domin ta ne Allah ya halicci dan Adam. An haifi Fatimatuz Zahra ne ranar Juma’a 20 ga watan Jimada Thani a shekara ta biyar bayan wahayi. Mahaifinta shi ne Manzon Allah Muhammad dan Abdullahi, cikamakon Annabawa da Manzanni, rahama ga talikai. Mahaifiyarta kuwa ita ce; Nana Khadijatul Kubra (AS) matar Manzo (S) ta farko, wacce ta fara amsa kiran Manzo. Sannan kuma ta bai wa wannan addini muhimmiyar gudummawar da ba za a taba mantawa da ita ba har abada. Manzo (S) ya ce...

HAIHUWAR SAYYIDA FATIMA AL-ZAHRA (A.S)

Image
An haifi Fatima al-Zahra (a.s) ne a ranar juma'a, Ashirin ga watan Jimada Sani, shekaru biyar bayan aiko Annabi. Bayan haihuwar Manzon Allah (s.a.w.a) ya amshi 'yarsa da farin ciki da amincewa, ya kuma sa mata suna  Fatima . An haifeta kuma ta tashi a gidan Annabci, ta tarbiyyantu a inuwar wahayi, ta kuma sha kaunar imani da kyawawan dabi'u daga Khadija. Fatima ta kasance mai dauke da ruhin Manzon Allah (s.a.w.a) da dabi'unsa, don haka ta zama mai gado da kuma tsananin kama da shi, har ma A'isha ta taba cewa: "Ban ga wanda ya fi kama da Manzon Allah (s.a.w.a) a rashin magana da kyauta fiye da Fatima 'yar Manzon Allah ba, a tsayuwarta da zamanta. Ta kasance idan ta shiga wajen Annabi (s.a.w.a) ya kan mike ya tarbe ta, ya zaunar da ita a wurin zamansa. Haka nan idan Annabi ya shiga gare ta, ta kan mike daga wajen zamanta ta tarbe shi, ta zaunar da shi a wajen zamanta (1) " Allah Ya so Fatima ta fara yarintarta a wani yanayi mafi tsananin wahala da kuntat...