BA ABIN MAMAKI BANE DON AN SAKI ZAKZAKY DAGA BAKIN MAQIYIN SHI,A.
Daga Alkalamin Datti Assalafiy Jiya kotu a Kaduna ta wanke Amirul Jaish na rundinar shi'ah (IMN) Ibrahim Yakubu Zakzaky daga tuhumar da Gwamnatin jihar Kaduna ta masa, biyo bayan abinda ya faru a Gazwatu Hussainiyyah Zaria da sojojin janar Buratai a 2015 Ni abinda na fahimta lokacin da Gwamnati ta gindaya masa ne kawai yayi ta sakeshi da kuma tasirin da Zakzaky yake dashi a cikin wannan Gwamnatin, amma ba wai don ta rasa hujjar da zata cigaba da tsareshi ba Sannan bayan matakin da kotun Kaduna ta zartar, har ila yau inda ace Gwamnatin Kaduna tana da niyyar cigaba da garkame Zakzaky da tayi hakan ta hanyar daukaka kara a kotun tarayya dake Abuja, kamar yadda dokar kasa ta tanadar Zakzaky yana da manyan mutane a Kasarnan wanda suna da tasirin da zasu iya nema masa alfarma har a gurin shugaban Kasa, idan baku sani ba Zakzaky yana da Manyan Ministoci har guda biyu a cikin wannan Gwamnatin wanda a baya har muzahara suna fita kafin a kafa Gwamnatin Buhari a 2015 Gareka Musulmi Ahlussunna...